Posts

Showing posts from September, 2017

SOYAYYAR MANZON ALLAH (SAWW)

SOYAYYAR MANZON ALLAH (SAWW). ************************************* SON ANNABI (saww) wani hali ne ko dabi'a wanda babu irinsa duk acikin halayen da 'Dan Adam zai iya siffantuwa dasu. Zuciyar da aka tarbiyyantar da ita bisa son Annabi (saww) takan Mance da duk wani abinda ba SHI ba. Kuma bata iya yin wani abu sai cikin koyi dashi. Zuciyar da ta riga ta gaurayu da SON ANNABI (saww) ta kan kasance batta ji, batta gani sai da SHI. Kuma bata yin kowacce Mu'amalar da zata nisantar da ita daga gareshi. Har ta kan kai matsayin yadda ba zata rayu ba, sai da Tunaninsa (sallallahu alaihi wa alihi wa sallam). MISALI : daga cikin Sahabbai akwai THAWBAAN (rta) wanda ya kasance ba ya iya jin dadi arayuwarsa, har sai yazo ya kalli Manzon Allah (saww). Tsawon dare (Awa 12) yayi yawa agareshi. Ba zai iya daurewa har gari ya waye bai ga Annabi ba (saww). Thawbaanu yakan kasa yin barci cikin dare, har sai yazo ya kalli gidan da Manzon Allah (saww) yake ciki. * Sayyiduna KHALID BN WAL

BABBAN TASHIN HANKALI

BABBAN TASHIN HANKALI!!! ***************************** Hadisi ne zan karanta muku daga Zauren Fiqhu Amma ina neman alfarma guda 'daya awajenku kafin ku karanta hadisin nan... Alfarmar da nake nema awajenku ita ce, ku tsayar da duk abinda kukeyi, ku nutsu ku karantashi da kyau. Domin na tabbata sai ya girgiza zuciyar duk wani mai Imani BISMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM. Tsira da aminci su tabbata bisa Annabin Qarshe, da dukkan Iyalansa da Sahabbai baki daya. Yazeedur Raqqaashiy ya karbo hadisin daga Anas bn Malik (ra) yana cewa: Watarana Mala'ika Jibreelu (as) yazo wajen Manzon Allah (saww) awani lokacin da bai saba zuwa masa ba. Yazo, gaba dayan launin fuskarsa ya chanza. Sai Manzon Allah (saww) yace masa "MAI YASA NAGA LAUNIN FUSKARKA DUK YA CHANJA HAKA?". Yace "Ya Muhammadu (saww) nazo maka ne awannan lokacin da Allah yayi Umurni da Masu hura wuta suci gaba da Hura ta. Duk wanda yasan cewa Jahannama gaskiya ce, Wuta gaskiya ce, Azabar Qabari gaskiya ce, ku