Posts

Showing posts with the label sahabah

LABARIN UMMU MALIK (RTA)

Akwai Wata Mata mai suna Ummu Malik ta kasance tana hidimta ma Manzon Allah (saww). Watarana ta zuba Man girki acikin Salka sannan ta tafi dashi ta kai masa (saww). To rannan ta wayi gari batta da Man gyadan ya Qare. Kuma gashi 'Ya'yanta suna bukatarsa zasu ci abinci. Da taje ta dauko Salkar sai ta tarar da ita acike Fal da man gyada. Ta dauko ta bama yaranta suka ci abinci dashi.. Ta kasance duk lokacin da take bukatar Mai agidanta, da ta dauko salkar sai ta tarar da ita acike Gal da mai. Rannan kawai sai ta juye man, ta tatse Salkar gaba daya... Tun daga ranar sai ta deba ganin Komai acikin salkar. Don haka taje ta sanar da Manzon Allah (saww). Sai yace mata : "DA ACHE BAKI TATSESHI BA, DA SAI YA ISHEKI HAR TSAWON RAYUWARKI". Acikin wata ruwayar kuma ance da ta koma gida sai taga Salkar man gyadar kamar ba'a juye ba.  Don haka sai hankalinta ya tashi. Ta dawo wajen  Manzon Allah (saww) Tace masa "Ya Rasulallahi ko an saukar da wata ayah. e game dani?...

GWARZON MUSULUNCI SALMANUL FARISIY (RA)

Sayyiduna Salmanul Farisy shine Sahabin da yafi dukkan Sahabbai yawan shekaru aduniya. Domin kuwa yafi shekara 100 yana jiran Zuwan Manzon Allah (saww). Wasu daga cikin Malaman tarihi sunce Shekara 170 ya ayu aduniya. Amma wasu kuma Sunce ya haura shekaru 300 ma yana raye. Watakil wadanda suka ce ya haura shekara 300 din zancensu yana da Qarfi domin kuwa Salmanul Farisy ya zauna awajen Manyan Malaman addinin Kirista masu yawa. Lokacin da ya gudo daga garinsu ya taho garin Shaam (Syria) sai ya tambayi mutanen garin cewa su nuna masa Babban Malamin addinin Nasaara (Kiristanci) Saboda alokacin nan musulunci bai bayyana ba. Sai suka nuna masa babban Paada (Bishop) na garin. Yaje ya zauna tare dashi tsawon shekaru, har mutumin nan ya tsufa basu rabu ba. har zuwa lokacin da Paadan nan ya rasu. Bayan ya rasu, Sai aka nada magajinsa. Sai Salmanul Farisy ya zauna tare da wannan magajin nasa tsawon shekaru har shima yazo rasuwa. Da yazo rasuwa sai Sayyiduna Salmanu ya tambayeshi shin Yanzu...