Posts

Showing posts from November, 2020

GORON JUMA'AH (20/11/2020)

Zuwa ga 'Yan uwa Musulmai masu yin rubuce-rubuce akan Social Media, da masu yin magana ko wa'azi a masallatai dal kafofin watsa labarai, musamman Malamai da 'yan siyasa.  Ya zama wajibi duk sanda zamuyi magana akan wani mutum ko wasu mutane mu rika yin adalci tare da lura da wasu abubuwa kamar haka : - Kar ka manta cewar shima musulmi ne, kuma baka da tabbacin cewar kai kafishi matsayi agun Allah.  - Ka rika tuna cewar Manzon Allah (saww) yace : "Duk wanda yake bibiyar laifin wani musulmi, shima sai Allah ya bibiyi laifukansa, kuma duk wanda Allah ya bibiyi laifukansa to sai ya kunyatar dashi koda atsakar gidansa ne". - Kar ka manta cewar idan kayi masa karya ko Qage, tofa bazaka mutu ba, har sai Allah ya jarrabeka ka aikata irin laifin da kake tuhumarsa akai.  - Kar ka manta cewar duk lokacin daka shagaltu da kallon laifukan mutane don yin tonon silili garesu, kai kuma sai Allah ya bayyanar da boyayyun laifukanka, wani lokacin ma har duk wani abin kunyar da iyaye

KAMBUN IDO (MAITA) DA HANYOYIN MAGANCETA DAGA ALQUR'ANI DA SUNNAH

ZAUREN FIQHU: KAMBUN IDO (MAITA) DA YADDA AKE MAGANCETA (01) BISMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM. Salati da aminci su tabbata bisa Annabin da aka bama Saba'ul Mathaniy da kuma Alqur'ani mai girma, Shugaban Masu fararen gabbai aranar Alqiyamah. Tare da iyalan gidansa inuwar al'ummah, da Sahabbansa yardaddu. Mun dade muna magana akan matsalar da ta shafi Massul Jinn (shafar Aljanu), Sihiri, da kuma Al-Ainu (kambun ido) ko Maita. Shi yasa yau na kuduri aniyar zan kawo mana wasu hanyoyi guda biyu ko uku wadanda za'a iya bi domin magance matsalar. Ita dai matsalar Kambun ido gaske ce ba Qarya ba. Domin Manzon Allah (saww) yayi bayaninta Qarara acikin hadisai da dama. Har ma yace "BAYAN QADDARAR ALLAH MADAUKAKIN SARKI, BABU ABINDA YAFI HALLAKAR DA AL'UMMATA FIYE DA KAMBUN IDO". Kuma yace "DA ACHE AKWAI ABINDA KE RIGA QADDARA AFKAWA KAN MUTUM, TO DA KAMBUN IDO YA RIGATA". Mafiya yawan masu Kambun ido, basu san ma suna dashi ba. Wadanda kuma suka san cewa suna d

JINNIYYATUL ASHIQAH (ALJANAR SOYAYYA)

Ita wannan Aljanar kamar yadda muka sha yin bayani ashekarun baya anan Shafin Zauren Fiqhu, yanayin shafarta da kuma Muguntar da take yiwa 'Dan Adam kusan irin na JINNUL ASHIQ ne. Sai dai ita har ta zarce Jinnul Ashiq wajen Mugunta da cin zalin 'Dan Adam.  JINNIYYATUL ASHIQAH Aljana ce Mace wacce takan shiga Jikin Mazajen Bil Adam bisa dalilin soyayya, (wato hujjarta wajen shuga jikinsu kenan wai sonsu takeyi).  Irin wannan Aljanar ayawancin lokuta takan yi kokarin dulmiyar da 'Dan Adam din cikin hallaka da sa'bon Allah  ta hanyar chanza masa dabi'u daga Kyawawa zuwa munana.. Wani ma takan hanashi gudanar da ibadunsa kamar sallah ko Azumi ko karatun Alqur'ani da sauransu.  Wani lokacin takan fara yin Zina da Mutum tun yana yaro Qarami. Wani ma zaka ga shekarunsa basu wuce biyar ko shida ba,  amma ahakan zata zo ta rika saduwa dashi. Irin wadannan Shaitanun sukan dauke Mutum su tafi dashi acikin mafarki don biyan bukatar kansu. Misali akwai wani yaro wanda ita ta

LUWADI (HOMO) ILLOLINSA DA HUKUNCE-HUKUNCENSA

Luwadi da Madigo yanzu awannan zamanin sun zama kamar ruwan dare atsakanin Matasa maza da mata. Sun biye ma sha'awar irin ta shaitanci wacce ta mamaye zukatansu, Sun afka cikin mafi Qazantar laifin da aka taba aikatawa adoron Qasa.  Don haka muka zakulo wata nasiha wacce muka taba rubuta ma wani matashi anan zauren fiqhu aranar 7-Jan-2015. (Karkashin tambaya ta 1477). Gata nan kamar haka: Hakika aduk cikin nau'o'in zina da dangoginta, Luwadi shine mafi Muni, kuma mafi Qazanta. Kamar yadda Allah yake gaya mana acikin Alqur'ani: " KA TUNA LOKACIN DA ANNABI LUUT YACE WA MUTANENSA    "MAI YASA KUKE ZUWA MA ALFASHA?  BABU   WANDA YA RIGAYEKU (AIKATA WANNAN) DAGA CIKIN TALIKAI".   "KUNA ZUWA WA MAZAJE MAIMAKON MATAYE TA FANNIN SHA'AWARKU   BARI DAI KU MUTANE NE MASU TSANANIN BARNA".  (A'araf ayah ta 80). Kuma saboda munin laifinsu shi yasa Allah yayi musu azabar da bai taba yima kowa kafinsu ba. Allah ya aiko da Mala'iku suka ciccibe garin