Posts

Showing posts from May, 2016

CIKIN QABARIN MUMINI

Ranar da aka sanya Mumini cikin Qabarinsa, rana ce mafi Muhimmanci gareshi. Rana ce wacce zai fita daga gidan wahala da Qunci da bakin ciki (wato duniya). Zai koma zuwa ga gidan hutu da yalwa da farin ciki. Rana ce wacce Mumini zai fara girbar alkhairin da ya shuka.. Wato sallolinsa da azuminsa da sadakokinsa da Zikiransa wadanda ya gabatar. Rana ce wacce Ubangijinsa zai cika masa alkawarin da yayi masa.. Wato Alkawarin cewa zai, shigar dashi cikin ni'imarsa mutukar dai yayi imani kuma ya aikata ayyuka na Kwarai. Rana ce wacce zai rabu da danginsa da iyalansa da dukiyoyinsa, Zai shiga cikin Ni'imar Ubangijinsa, da kuma arzikin da ba ya Qarewa. Rana ce wacce Mumini zai chiza yatsansa, yana burin inama za'a bashi damar dawowa duniya domin ya aikata wasu Qarin ayyukan alkhairi. Saboda irin girmamawar da ya samu awajen Ubangijinsa. Rana ce wacce dukkan 'Yan uwansa da danginsa suna cikin Kuka, da Bakin ciki. Amma shi kuwa yana cikin farin ciki da annashuwa. Wasu daga

CIKIN QABARIN MUMINI

Ranar da aka sanya Mumini cikin Qabarinsa, rana ce mafi Muhimmanci gareshi. Rana ce wacce zai fita daga gidan wahala da Qunci da bakin ciki (wato duniya). Zai koma zuwa ga gidan hutu da yalwa da farin ciki. Rana ce wacce Mumini zai fara girbar alkhairin da ya shuka.. Wato sallolinsa da azuminsa da sadakokinsa da Zikiransa wadanda ya gabatar. Rana ce wacce Ubangijinsa zai cika masa alkawarin da yayi masa.. Wato Alkawarin cewa zai, shigar dashi cikin ni'imarsa mutukar dai yayi imani kuma ya aikata ayyuka na Kwarai. Rana ce wacce zai rabu da danginsa da iyalansa da dukiyoyinsa, Zai shiga cikin Ni'imar Ubangijinsa, da kuma arzikin da ba ya Qarewa. Rana ce wacce Mumini zai chiza yatsansa, yana burin inama za'a bashi damar dawowa duniya domin ya aikata wasu Qarin ayyukan alkhairi. Saboda irin girmamawar da ya samu awajen Ubangijinsa. Rana ce wacce dukkan 'Yan uwansa da danginsa suna cikin Kuka, da Bakin ciki. Amma shi kuwa yana cikin farin ciki da annashuwa. Wasu daga

HANYOYIN SAMUN SHIGA ALJANNAH (043)

CIKAWA DA KYAKKYAWAN AIKI ********************************** Hadisi daga Huzaifah Ibnul Yamaan (rta) yace : "Na shiga wajen Manzon Allah (saww) alokacin jinyarsa wacce ya rasu acikinta. Sai yace "ZAUNAR DANI". Sai Sayyiduna Aliyu (ra) ya zaunar dashi ya jinginar dashi zuwa ga Qirjinsa. Sai nace ma Aliyu din "Ya Abu Hamza, Ka kwana kana jinyarsa (wato ina so nima ka barni inyi jinyar Manzon Allah). Sai Manzon Allah (saww) yace: "YA KAI HUZAIFAH, AI ALIYU YAFI KA CHANCHANTA DA WANNAN AIKIN..  MATSO NAN KUSA DANI". (Da na Matso kusa dashi sai yace). "YA HUZAIFAH! DUK WANDA "LA ILAHA ILLAL LAAHU" TA ZAMANTO AIKINSA NA KARSHE KAFIN MUTUWARSA, TO ZAI SHIGA ALJANNAH. KO KUMA ZA'A GAFARTA MASA. "YA HUZAIFAH! DUK WANDA AKA CIKA MASA (AIKINSA NA KARSHE) KAFIN MUTUWARSA DA AZUMIN RANA GUDA DOMIN NEMAN YARDAR ALLAH, ZAI, SHIGA ALJANNAH, KO KUMA ZA'A GAFARTA MASA". "YA HUZAIFAH! DUK WANDA AKA CIKA MASA AIKINSA NA KARSHE KAF

HUKUNCIN MASU SAIDA SIGARI DA KAYAN MAYE

TAMBAYA TA 1934 ******************** ASSALAMU ALAIKUM MAL DON GIRMAN ALLAH A'ANSA MIN TAMBAYA. YAYA HUKUNCI MAI SAYAR DA SIGARI DA KWAYOYIN SA MAYE A MUSULINCI? NAGODE ALLAH YAKA DA ALHERI AMIN DAGA DALIBINKA SHAFIU BELLO ANKA ZAMF WASSALAM AMSA ******* Wa alaikumus salam wa rahmatullahi wa barakatuhu. Duk abinda amfani dashi ya zama Haramun, to hakanan sayar dashi ko dakonsa ko shukawa, ko girbewa ko sarrafawa duk HARAMUN ne. Kuma dukkan abinda ke sanya maye, sunansa giya ne. Kuma Allah ya haramta giya, ya kuma tsine ma masu yinta da masu dakonta da masu shayar da ita da masu sayar da ita. Ita kuwa Sigari kayan Almubazzaranci ce. Kuma Allah yace su Amubazzarai 'Yan uwan shaitan ne. Shi kuwa shaitan ya butulce ma Ubangijinsa ne. Hukuncin mai sayar da irin wadannan abubuwan shine ya aikata HARAM. Domin kuwa Allah yace "KUYI TAIMAKEKENIYA BISA BIN ALLAH DA KUMA TAQWA. KADA KUYI TAIMAKEKENIYA CIKIN SA'BON ALLAH DA QETARE IYAKOKINSA". Sayar da Sigari da kay

BASU SON 'YARSU TA AURI TALAKA

TAMBAYA TA 1928 ******************** Assalamullahi alaika, Allah y qara lpy d rayuwa mai ampani. amin. mallam dan Allah ataimaka mun da addu'ar dazan dunga yi. Mun kasance muna son juna d saurayina, kuma aure ya kawoshi. Amma wadanda nake zaune awajensu basa so wai saboda malamin makaranta ne har sukancemin wai "me nasama yaci bare yaba naqasa" Ni kuma nafi son yin auren kwanciyar hankali da ganin mutuncin juna koda kullum sai ya fita zai samo. Dan Allah mallam ataimaka mun da addu'ar dazan keyi kan Allah ya Fahimtar dasu su goya mun baya. AMSA ******* Wa alaikis salam wa rahmatullahi wa barakatuhu. Abinda zakiyi da farko shine Ki dogara ga Allah, domin duk wanda ya dogara ga Allah sai Allah din ya isar masa akan dukkan damuwarsa. Ki yawaita yin addu'ar nan ta Annabi Yunus (as) wacce Manzon Allah (saww) yace "BABU WANI WANDA YAKE CIKIN BAKIN CIKI DA ZAI KARANTA-TA FACHE SAI ALLAH YA YAYE MASA". Addu'ar ita ce "LA ILAHA ILLA ANTA SUBHAN