Posts

Showing posts from November, 2017

HALAYEN MASU TSORON ALLAH (02).

BISMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM Ya Allah yi salati da aminci mafi wanzuwa bisa Babban Masoyin nan naka wanda babu kamarsa. Shugabanmu Annabi Muhammadu tare da iyalan gidansa amintattu, da Sahabbansa masu daraja. Daliban Zauren Fiqhu, wannan shine darasi na biyu acikin Maudhu'in da muke bayani akan Halaye ko kuma dabi'un magabata na kwarai dangane da yadda tsoron azabar Allah ako yaushe. Duk da cewar su din mutane ne masu mutukar Son Allah da Manzonsa da kuma tsayawa akan ibadah dare da rana. Kuma muna fadin halayensu ne domin muji muyi amfani dashi, mu kwaikwayesu gwargwadon ikonmu. Yazeed bn Hushib (rah) yace: "Ban taba ganin mutane masu tsananin tsoron Allah kamar Hasanul Basariy da kuma Umar bn Abdil-Azeez ba. Saboda tsananin tsoron azabar Allah, kai kace dominsu kadai aka halicci Wutar!". Shi dai Umar bn Abdil-Azeez yana daga cikin Banu Umayyah. Kuma tun daga ranar da ya karbi Khalifancin daular Musulunci bai taba kwanciya yayi barcin dare akan katifarsa ba. Ya

RANAR DA YABAR DUNIYA (2)

RANAR DA YA BAR DUNIYA (2) ******************************* Sayyiduna Anas bn Malik (ra) ya ruwaito cewa "Yayin da Annabi (saww) jinyarsa tayi nauyi, ya kasance Zafin ciwo yakan lullubeshi. Sai Nana Fatimah (as) tace "WAYYO WAHALAR BABANA!!". Sai Annabi (saww) yace mata "BAYAN YAU DIN NAN BABU SAURAN WATA WAHALA AKAN BABANKI". Yayin da Annabi (saww) ya rasu, sai Nana Fatimah tace "Wayyo Mahaifina! Ya amsa kiran Ubangijin da ya kirashi!... Wayyo Mahaifina! Aljannar Firdausi ce Masaukinsa. Wayyo Mahaifina, Zuwa ga Mala'ika Jibreelu muke mika Ta'aziyyarsa!". Yayin da aka binneshi kuma sai Nana Fatimah tace ma Sahabbai "Shin Zukatanku sunyi muku da'di yayin da kuka Watsa Qasa bisa Manzon Allah (saww) ?". Imamul Bukhariy ne ya ruwaitoshi. Allahu Akbar!!! Nana Fatimah muna yi miki Ta'aziyyar Abbanki wanda babu Musibar da tafi rashinsa girma akan Mumini mai cikakken imani. Tunda ake rasuwa ba'a ta'ba yin irin tasa ba

DUWATSUN DAKE SONSHI (SAWW) - 1

DUWATSUN DAKE SONSHI (SAWW) 1 ************************************* Yana daga cikin Khasa'isu na Annabi Muhammadu (sallal Laahu alaihi wa aalihi wa sallam) cewa Allah ya sanya soyayyarsa azukatan halittu masu motsi har ma marassa motsi. Mun kawo muku Qissar duwatsun dake yin gaisuwa gareshi tun tasowarsa agarin Makkah. Kuma mun gaya muku labarin wani dutsen dake gaisheshi bayan an fara yi masa wahayi. Sannan mun gaya muku Qissar da aka ruwaito daga Sayyiduna Aliyu bn Abi Talib (rta) game da duwatsu da bishiyoyin dake yin gaisuwa ga Manzon Allah (saww). Daga cikin duwatsun duniya wadanda soyayyarsu ga Manzon Allah (saww) ta bayyana Qarara afili, dutsen Uhudu yana kan gaba.. Sayyiduna Anas bn Malik (ra) yace "Manzon Allah (sallal Lahu alaihi wa aalihi wa sallam) ya hau kan Dutsen Uhudu tare da Abubakar da Umar da Uthman (Radhiyallahu anhum). Sai dutsen yayi girgiza dasu (Saboda Shauqin jin tafin Qafar Manzon Allah akansa). Sai Manzon Allah (saww) ya bugeshi da Qafarsa mai

DUWATSUN DAKE SONSHI (SAWW) 2

DUWATSUN DAKE SONSHI (SAWW) 2 ************************************* Babban Malamin Hadisin nan a Mazhabin Malikiyyah, wato Alqadhiy 'Iyadh ya ruwaito acikin ASH-SHIFA cewa : Manzon Allah (saww) ya hau kan dutsen Thabeer Lokacin da Kafirai suke nemansa zasu kasheshi. Sai dutsen yayi magana dashi yace masa "Sauka Ya Rasulallahi. Domin ni ina tsoron kada su kasheka akan bayana, Kuma Allah yayi mun azaba". Shi kuma Dutsen Hira'u yace "Taho gareni Ya Ma'aikin Allah". Dutsen Thabeer da Dutsen Hira'u makobtan juna ne. Suna daura da juna, amma akwai wani kwari atsakaninsu. ADUBA ANWARUL MUHAMMADIYYAH ta Shaikh Yusufun Nabhaniy (rah) akan shafi na 275. Kunji fa yadda duwatsu suke gasar nuna kishinsu da soyayyarsu gareshi (sallal Lahu alaihi wa aalihi wa sallam). Kaima kayi hankali da zuciyarka kada ta rudeka ka rika jin Qaikayi azuciyarka idan kaji ambatonsa.. Domin hakika Imani ba ya tabbata sai da Tsantsar Soyayyar Annabi Muhammadu (sallal Lahu alai