Posts

Showing posts from April, 2019

MU SAN ANNABINMU (26)

Salati da amincin Allah su tabbata bisa Shugabanmu Annabi Muhammadu tare da iyalan gidansa tsarkaka da Sahabbansa da dukkan mabiyansu da kyautatawa har zuwa ranar sakamako. Acikin wannan darasin na Zauren Fiqhu zamu dora daga inda muka tsaya acikin tarihin Manzon Rahama (sallal Lahu alaihi wa aalihi wa sallam). YAQIN HAMRA'UL ASAD : Washegarin dawowa daga yaqin uhudu sai Manzon Allah (saww) yayi tunanin watakil mushrikan Quraishawa su sake kawo hari garin madeenah don haka yayi nufin fita domin sake tararsu a sake wani sabon gumurzu don a nuna musu cewa har yanzu fa musulunci yana nan da Qarfinsa. Ashe kuwa shi Abu Sufyan shugaban dakarun Quraishawa ya daura niyyar dawowa din don Qara kawowa hari akan Musulmai, akan hanyarsa sai ya hadu da wani mutum mai suna Ma'abadu 'dan Ubayyu Alkhuza'iy. Sai Abu Sufyan din ya tambayeshi "Meye labarin abinda ke bayanka?". Sai yace masa "Ya kai Abu Sufyan, yi sauri ka guje daga garesu domin hakika sun tanadi makama

LABARIN CIKIN QABARI

Ibnu Abid Dunya ya ruwaito ta hanyar Hammadu bn Salamah, shi kuma ya karbo daga Hisham bn 'Urwah, shi kuma daga Babansa yana cewa : "Watarana wani mahayin doki yana tafiya atsakanin garin Makkah da Madeenah sai gashi kusa da wata Maqabarta,  sai yaga wani mutum ya fito daga cikin Qabarinsa yana ci da Wuta!!. Ga kuma Qarafuna an daddaureshi dasu. Sai yace "Ya kai bawan Allah! Hure min wutar nan! Hure min wutar nan!". Nan take sai ga wani ya sake fitowa ta cikin wannan Qabarin, yabi wancan din yana cewa "Ya kai bawan Allah kada ka bushe masa (wutar nan)!" Nan take shi wannan mahayin dokin ya suma akan dokin nasa. Kuma dokin yaci gaba da tafiya dashi ahaka har sai da ya kaishi wajen wata rijiya. Yayin da ya farka sai yaga duk gashin dake kansa ya juye ya zama furfura fari fat tamkar auduga! Yaje ya bama Sayyiduna Uthman bn Affan (ra) labarin abinda ya faru (Zamanin Khalifancinsa ne). Sai shi Sayyiduna Uthman din ya hana mutum ya rika yin tafiya shi ka'

MU SAN ANNABINMU (25)

Da sunan Allah mai rahama mai jin qai, salati da amincin Allah su tabbata bisa Shugabanmu Annabi Muhammadu tare da iyalan gidansa tsarkaka da Sahabbansa shiryayyu. YAQIN BANU QAINUQA'A : Banu Qainuqa'a sunan wata Qabila ne daga cikin Qabilun yahudawan madeenah wadanda Manzon Allah (sallal Lahu alaihi wa aalihi wa sallam) ya qulla alkawarin zan lafiya dasu tun farkon zuwansa garin. Nasarar da Manzon Allah (saww) ya samu a yaqin badar ta basu haushi, don haka sai suka fito fili suna bayyana qiyayyarsu ga Musulmai da kuma soyayyarsu ga mushrikan Quraishawa. Kuma sun kasance suna gadara da Qarfin tattalin arziki kasancewarsu masu sana'ar zinare ne. Suna cin mutuncin jama'ar musulmai, suna yi musu izgili har dai watarana suka yiwa wata mace musulma tsirara a kasuwarsu, ta nemi taimako awajen wani musulmi ya taimaka mata ya kashe bayahuden da ya zalunceta. Sai sauran yahudawan suka taru akansa (shi Musulmin) suka kasheshi. Wannan shine tushen yaqin. Kuma Manzon Allah (sa

RANAR RABON TAKARDU!!!

Ranar da za'ayi rabon takardu, rana ce wacce hankula ke tashi.. Idanuwa suna kuka amma babu zubar hawaye...! Mutane zasu kasance kaso uku ne awannan lokacin : # Akwai wadanda ba za'a basu littafi ba. Wato ba za'a yi musu hisabi ba. Kamar Annabawa kenan (as) da manyan Salihan bayin Allah da Siddiqai da Shahidai. # Akwai wadanda zasu karbi littafinsu ta hannun dama. Sune wadanda za'ayi musu hisabi sassauka. Wato ba za'a duba laifukansu ba. Farkon wanda zai karbi Littafinsa da hannun dama shine Sayyiduna Umar bn Khattab (rta). Kamar yadda hadisi ya fada. # Akwai wadanda zasu karbi littafinsu ta hannun haggu. Acikin wata ayar ma Allah yace zasu karba ne ta baya. Wato Mala'iku zasu sanya hannunsu na hagu su fasa musu Qirjinsu dashi, sannan su zaroshi ta baya, Sannan a miko musu littafin nasu. Za'a ce ma kowanne daga cikinsu " KARANTA LITTAFINKA DA KANKA .... " A sannan ne Dan Adam zai tuno da dukkan abinda ya aikata a rayuwarsa ta duniya.. Wat

LABARIN DAMO YANKAKKE

DAGA ZAUREN FIQHU : Wani Balaraben Qauye ya farauto Damo (alligator) ya shigo gari sai yaga Manzon Allah (saww) tare da wasu Jama'a yana yi musu wa'azi. Da yaga haka sai ya tambayi mutane "Wannan mutumin fa? wanene?". Sai akace masa "AI ANNABI NE". Saboda haka sai Balaraben Qauyen nan ya rika keta tsakanin jama'a, har sai da yazo ya tsaya agaban Manzon Allah (saww). Sannan yace: "Na rantse da lata da uzza (sunayen gumakansa ne) babu mutumin da na tsaneshi fiye da kai, Ba don kar mutanena su washeni ba, da sai na kasheka". Sayyiduna Umar bn Khattab (ra) zai zare takobi ya kasheshi sai Manzon Allah (saww) ya hanashi. Balaraben Qauyen nan ya fito da damonsa (yankakke) daga cikin jakarsa, ya jefar agaban Manzon Allah (saww) sannan yace: "Na rantse da lata da uzza ba zan bada gaskiya gareka ba, har sai wannan yankakken damon yayi Imani dakai". Sai Manzon Allah (saww) yace "YA KAI DAMO!!". Sai Damon ya amsa acikin harshe

MAGANIN TSAGEWAR FATAR TAFIN HANNU DA SAURAN CIWUKAN DAJI :

TAMBAYA TA 2621 ******************* Assalamu Alaikum, Malam barka da rana ya iyali? Allah saka maku da aljanar firdaus akan taimakon dakukeyi amin. Malam yarona ne  yake  fama da kuraje a tafukan hannun shi   kurajan suna fitowane kamar bororon Wuta, wani lokaci kuma sai sufito kanana ko kuma haka kawai sai hannuwan su rinka tsagewa kamar ya yanke kuma suna Mashi kaikai Dan wani lokaci kaikain yakan hanashi bacci sosai idan kuma ya Sosa sai su rinka fitar da jini.Malam dan  Allah ataimaka mana, daga  dalibarku. AMSA ******* Wa alaikis salam wa rahmatullah. Irin wadannan chutukan fata ne kuma basu rasa alaqah da ciwon daji irin na fata. Amma ga wasu abubuwa nan ki jarrabah. 1. Ki samu lalle (irin wanda kuke yin Qunshi dashi) ki kwaba da ruwa amma ki sanya man zaitun kamar cokali guda aciki. Sai kiyi masa Qunshi a hannayen nasa. Lalle yana maganin mafiya yawan ciwukan fata. Kici gaba da yi masa Qunshin duk bayan sati biyu. In shaAllah cikin Qankanin lokaci Qirajen zasu dena fitow

MADUBIN DUBAWA (70)

Yau madubin namu zai waiga baya ne ya dauko mana wani abu daga rayuwar magabatanmu wato tabi'ai da tabi'ut tabi'un. Daga cikin magabata akwai wadanda tsoron wutar lahira da kuma tunaninta yasa suka haramta wa kansu yin dariya anan gidan duniya. Isma'eel As-Suddiy (rah) yace "Lokacin da Hajjaju bn Yusuf (wani azzalumin gwamna ne) yasa aka kamo masa babban Malamin tabi'ai din nan mai suna Sa'eed bn Jubair kafin ya kasheshi sai ya tambayeshi cewa "Labari ya sameni cewa wai kai baka ta'ba yin dariya ba tunda kake!". Sai Sa'eed bn Jubair (rah) yace masa "Ta yaya zan rika dariya alhali an riga an hura jahannama, Kuma Qukuman cikinta an riga an kakkafasu, Kuma Zabaniyawan cikinta an riga an tanadesu ? (Qukumi shine irin chain din da ake Qakaba musu a wuyansu lokacin da ake jibgarsu ana azabtar dasu. Zabaniyawa kuma sunan Mala'ikun nan ne Qarfafa guda goma sha tara wadanda Allah ya tanadar dasu domin azabtar da 'yan wuta). Bayan H

MU SAN ANNABINMU (24)

Da Sunan Allah Mai Girma, salati da amincinsa su tabbata bisa bawansa mafi girma, Annabinmu Muhammadu tare da Iyalan gidansa tsarkaka da Sahabbansa masu girma. YAKOKIN ANNABI (SAWW) : Yakokin da Manzon Allah (saww) yayi azamaninsa, ba wai yana yinsu ne domin daukar fansa ko son zubar da jini ba. A'a yakokin nasa sun kasance ne domin mayar da kaidin abokan gaba da ladabtarwa ga duk wani mai ta'addanci, da kuma kira zuwa ga addinin Allah. Annabi (saww) yayi yakoki da dama kafin badar da kuma bayanta, domin amintar da garin Madeenah da kuma bayar da kariya gareta daga hare-haren kafirai. Akwai yakokin da ya samu halarta, sun kai kamar guda ashirun da bakwai ko da takwas. Akwai kuma wasu da dama wadanda bai je ba amma ya tura da rundunoni karkashin jagorancin amintattu daga cikin Sahabbansa. YAQIN BADAR : Manzon Allah (saww) ya samu labarin gabatowar wani ayarin fatauci na Quraishawa mai kunshe da rakuma dubu dauke da kayan fatauci, Kuma Abu Sufyan ne yake jagorantar tafiyar

MU SAN ANNABINMU (12)

Da sunan Allah Makadaici, Salati da aminci su tabbata ga Annabinmu tare da iylan gidansa tsarkaka da Sahabbansa da dukkan mabiyan bayansu da kyutatawa. Wannan shine ci gaban darasinmu na Zauren Fiqhu wanda acikinsa muke kawo muhimman lamura acikin tarihin Ma'aikinmu (sallal Lahu alaihi wa aalihi wa sallam). ZAMANSA A KOGON HIRA'U ***************************** Annabi (saww) ya kasance akowacce shekara yakan kebance kansa tsawon wata guda ya tafi kogon hira'u wanda ke kan Jabalun Nur ya zauna yana tunani cikin lamarin Ubangijinsa kuma yana ibadah (bautar Allah) bisa addinin Kakansa Annabi Ibrahim (alaihis salam). Wannan tun kafin ya cika shekaru arba'in aduniya kenan. Amma bayan ya cika 'dan shekara arba'in aduniya watarana yana zaune acikin kogon sai ya hangi siffar wata Halitta mai girman gaske ta cika dukkan sasanni. Ashe Shugaban Mala'iku ne wato Jibreelu (amincin Allah ya tabbata gareshi). Yazo ya rungumeshi zuwa jikinsa runguma mai tsanani sannan y

ILLOLIN SHAN TABAR WEEWI

Acikin 'yan shekarun nan da matasa suka lalata kansu ta hanyar amfani da miyagun kwayoyi, Tabar Weewi ita ce kan gaba fiye da dukkan miyagun Kwayoyin da matasan suke amfani dasu. Wannan yasa ZAUREN FIQHU ya gudanar da bincike akanta domin ganowa irin illolinta, da kuma yadda take aiki wajen ruguza lafiyar jikin masu ta'ammali da ita. SUNAYENTA ************* Kasancewar ana amfani da ita kusan adukkan nahiyoyin duniya, wannan yasa Tabar Weewi take da sunaye kala-kala kamar haka: WEEWI, Ganye, Marijuana, Indian Hemp, Ganja, Pot, Igbo, Weed, Canabees, Hasheesh, Texas Tea, da dai sauransu. ILLOLINTA *********** Ganyen tabar WEEWI yana kunshe da Sinadarai sama da guda Arba'in masu chutar da lafiyar 'Dan Adam. Daga cikinsu har da sinadarin TETRA-HYDRO-CANNABINOL (T.H.C.) wani mummunan sinadari ne wanda yake chanza ma kwakwalwar 'Dan Adam yanayin yadda take karbar sakonni da yadda take sarrafa su. Duk lokacin da mashayin Weewi ya Zuki hayakinta, shi wannan Mummunan

HANYOYIN KANKARAR ZUNUBAI (1)

TUBA DAGA DUKKAN ZUNUBAI Daliban Zauren Fiqhu da sauran jama'ar musulmai, Assalamu alaikum wa rahmatullahi wa barakatuhu. Wannan sabon jerin karatu ne wanda yake kunshe da wasu hanyoyin samun kankarar zunubai da lada mai yawa. Zai  rika zuwa muku tare da ayoyi da hadisai ingantattu. In shaAllah. Hanya ta farko wacce zaka bi amatsayinka na bawan Allah domin neman kusanci da mahaliccinka ita ce hanyar tuba daga duk wani zunubi da kasan kana aikatawa, Qananan zunubai da manyansu in dai ka tuba domin Allah, to zai karbi tubanka cikin karamcinsa kuma ya gafarta maka laifukanka. Ya fa'da acikin littafinsa mai girma yace : "KU TUBA ZUWA GA ALLAH BAKI DAYANKU YA KU MUMINAI, TSAMMANIN TABBAS ZAKU RABAUTA". Suratun Nur ayah ta 31. Kuma kada girman zunubanka ko kallon yawan laifukanka, ko laifukanki ya hanaka, ko ya hanaki tuba. Hakika babu abinda yake gagarar Ubangiji. Kada ku manta fa Allah yayi kira garemu ta hanyar Annabinsa (sallal Lahu alaihi wa aalihi wa sallam)

FA'IDODIN TSAMIYA DAGA ZAUREN FIQHU

Tsamiya wata bishiya ce wacce ake shukata kuma ana magani da ita tun kusan shekaru dubu uku da suka gaba. Kuma ana samunta acikin dazuzzukan nahiyarmu ta Afirka da kuma kudancin nahiyar Asia. Likitocin Musulunci sun dade suna amfani da 'ya'yan bishiyar domin magance larurori masu yawa, haka kuma ana amfani da ita wajen hada nau'o'in abinci da abinsha. 'Ya'yan wannan bishiya ta tsamiya suna kunshe da sinadarai masu yawa sosai wadanda ke Qara ma jikin Dan Adam amfani mai yawa.  Misali : - Vitamin A 151, Vitamin E, Vitamin B da kuma C. Sannan acikinta akwai Calcium, Potassium, thiamine, Tartaric Acid, Phosphorous, Proteins, Magnesium, Riboflavin. Haka kuma sabobbin ganyenta suna kunshe da sinadarin Sulfur da Calcium mai yawan gaske. Yanzu ga wasu fa'idodi ka'dan daga cikin dimbin abubuwan amfani dake cikin tsamiya : 1. CIWON ZUCIYA : Shan kunun tsamiya ko farau-farau (Juice) wanda aka yishi da tsamiya zai iya zama riga-kafi daga kamuwa da chutar hawan

MU SAN ANNABINMU (11)

Da sunan Allah Mamallakin komai da kowa, Salatinsa da amincinsa su tabbata ga Mabudin alkhairansa, Annabinmu Muhammadu tare da iyalan gidansa tsarkaka da Sahabbansa baki daya. SABUNTA GININ KA'ABAH ************************* Yayin da shekarun Manzon Allah (saww) suka cika talatin da biyar aduniya, anyi wani ruwa mai yawa acikin garin Makkah wanda ta sanadiyyar ambaliyarsa ya kwararo ya cika dakin Allah mai alfarma (KA'ABAH) har sai da bangwayenta suka tsattsage. Saboda tsoron rushewarta sai Quraishawa suka yanke shawara atsakaninsu cewa zasu rushe ginin sannan su sake mayar dashi kamar yadda yake. Tare da bayar da gudunmuwa daga mafi tsarkin dukiyarsu, sunyi nasarar mayar da ginin. To amma yayin da aka zo wajen mayar da Baqin dutsen nan (Hajarul Aswad) wanda ke maqale ajikin dakin Ka'abah, sai suka samu sa'bani atsakaninsu akan shin wanene zai dauki dutsen ya sanyashi awajensa, saboda alfahari da girman dake cikin wannan. Daga karshe sai suka yanke shawarar cewa du

MU SAN ANNABINMU (10)

Da Sunan Allah Masanin fili da boye, Salati da aminci su tabbata ga Ma'abocin Alqur'ani da Sab'ul Mathaniy, Annabinmu Muhammadu tare da iyalan gidansa da matayensa da dukkan Sahabbansa da Salihan bayin Allah baki dayansu. AURENSA DA NANA KHADIJAH (RA). Manzonmu (sallal Lahu alaihi wa aalihi wa sallam) tyn tasowarsa ya shahara da kyawawan halaye da dabi'u irin su gaskiya da rikon amana da hakuri da kyautatawa, da dukkan wasu halayen ababen yabawa. Ita kuma Nana Khadijah bintu Khuwailid (ra) wata Mace ce Ma'abociyar kyawu da daukakar nasaba ga kuma dukiya mai yawa wacce Allah ya bata a hannunta. Ta kasance tana bayarwa ana yi mata kasuwanci da dukiyarta ta hanyar aika Mazaje zuwa garuruwa masu nisa domin saye da sayarwa sannan a raba ribar da aka samu. To Nana Khadijah watarana ta gani acikin mafarkinta cewa rana ta sauko daga sama ta fa'do acikin dakinta, akan Qirjinta. Yayin da ta farka afirgice ta gaya ma wani Malami makarancin Attaura kuma 'Dan Baffant

MU SAN ANNABINMU (02)

MAHAIFANSA : Mahaifinsa shine Abdullahi 'dan AbdulMuttalibi 'dan Hashim. Yana daga mafiya kyawu da nagartar samarin zamaninsa. Mahaifiyarsa kuwa ita ce Nana Ãminatu (Az-Zuhriyyah) 'yar Wahbin 'dan Abdu Manaf 'dan Zuhrata. Ta fito daga dangi masu tsarki da nagarta da daukaka daga cikin dangogin larabawa Quraishawa. HAIHUWARSA : An haifi Shugabanmu Annabi Muhammadu (sallal Lahu alaihi wa aalihi wa sallam) ne a garin Makkah acikin unguwar banu Hashim, ranar litinin sha biyu (12) ga watan rabee'ul awwal ashekarar giwaye, wacce tazo daidai da 20 ga watana aprilu shekara ta 571 miladiyyah. An haifeshi ne maraya kasancewar mahaifinsa ya riga ya rasu tun yana da 'yan watanni acikin mahaifiyarsa. Kuma an haifeshi mai tsarki mai haske mai Qamshi, idonsa da tozali. Kuma ya sauka tare da haske mai girma wanda ya haskake garin makkah baki dayansa har garuruwa masu nisa. Kakansa Abdul Muttalibi ne ya ra'da masa wannan suna "MUHAMMADU" bisa ilhamar Ubang

MU SAN ANNABINMU (04)

Godiya ta tabbata ga Allah Mamallakin zukata da hankula, wanda ya zabi zukatan wasu daga cikin bayinsa kuma ya karkatar da zukatansu zuwa ga shagaltuwa da kokarin sani da koyi da neman cikar soyayyar Manzonsa wanda ya aiko zuwa ga dukkan halittu (saww). Salati da aminci su tabbata bisa Annabin da bai ta'ba magana bisa son rai ba, fache bisa wahayi daga Ubangijinsa. TSAGAWAR KIRJINSA : Kamar yadda muka ta'ba bayani acikin wani darasinmu na Zauren Fiqhu Whatsapp, an tsaga Kirjin Manzon Allah (sallal Lahu alaihi wa aalihi wa sallam) ne har sau hudu alokuta daban daban. Kuma ga takaitaccen bayanin yadda kowanne ya faru : NA FARKO : Lokacin da ya cika shekaru hudu aduniya, sai Ubangijinsa (SWT) ya turo masa Mala'iku guda biyu wato Jibreelu da Meeka'ilu (amincin Allah ya tabbata garesu). Suka zo suka tarar dashi alokacin yana kiwon tumakin Halimatus Sa'adiyyah tare da sauran yaranta. Mala'ikun nan suka kwantar dashi suka tsaga qirjinsa suka fito da zuciyarsa madau

MU SAN ANNABINMU (04)

Godiya ta tabbata ga Allah Mamallakin zukata da hankula, wanda ya zabi zukatan wasu daga cikin bayinsa kuma ya karkatar da zukatansu zuwa ga shagaltuwa da kokarin sani da koyi da neman cikar soyayyar Manzonsa wanda ya aiko zuwa ga dukkan halittu (saww). Salati da aminci su tabbata bisa Annabin da bai ta'ba magana bisa son rai ba, fache bisa wahayi daga Ubangijinsa. TSAGAWAR KIRJINSA : Kamar yadda muka ta'ba bayani acikin wani darasinmu na Zauren Fiqhu Whatsapp, an tsaga Kirjin Manzon Allah (sallal Lahu alaihi wa aalihi wa sallam) ne har sau hudu alokuta daban daban. Kuma ga takaitaccen bayanin yadda kowanne ya faru : NA FARKO : Lokacin da ya cika shekaru hudu aduniya, sai Ubangijinsa (SWT) ya turo masa Mala'iku guda biyu wato Jibreelu da Meeka'ilu (amincin Allah ya tabbata garesu). Suka zo suka tarar dashi alokacin yana kiwon tumakin Halimatus Sa'adiyyah tare da sauran yaranta. Mala'ikun nan suka kwantar dashi suka tsaga qirjinsa suka fito da zuciyarsa madau

MU SAN ANNABINMU (03)

Da sunan Allah Makadaici, Salati da aminci su tabbata bisa Fiyayyen Halittu tare da iyalan gidansa da Sahabbansa da dukkan bayin Allah Salihai. SHAYARWARSA (SAWW)  : Farkon wacce ta shayar dashi aduniya ita ce mahaifiyarsa Nana Aminatu 'yar Wahb, daga nan sai wata baiwar baffansa Abu Lahab wacce ake kira Thuwaibatul Aslamiyyah (rta) ta shayar dashi itama. Kuma dama Abu Lahab din ya 'yantar da ita tun bayan haihuwar Manzon Allah (saww) alokacin da tazo yin albishiri gareshi cewa Matar 'dan uwansa ta haifi 'da namiji. Sai kuma Haleematus Sa'adiyyah itama ta shayar dashi. Kuma ta dalilin wannan shayarwar ta samu daukaka da fifiko da yalwar arziki. Gidanta ya cika da albarka da arziki da ni'ima saboda albarkacin kasancewar Annabi (saww) tare da ita. Kuma yana daga cikin girmamawar da Allah yayi masa, dukkan matayen da suka shayar dashi sun karbi addininsa (saww). Koda yake akwai riwayar da tazo da akasin haka, amma riwayar musuluntar tasu tafi Qarfi kuma gareta

MU SAN ANNABINMU (23)

Da sunan Allah Makadaici abun bauta. Salati da amincinsa su tabbata ga babban bawansa, Annabinmu Muhammadu tare da iyalan gidansa da dukkan Sahabbansa. SHIRYA ZAMAN MADEENAH : Kamar yadda na fa'da muku acikin darasi na 22,  ainahin sunan garin Yathriba amma bayan isowar Manzon Allah (sallal Lahu alaihi wa aalihi wa sallam) sai sunanta ya koma "Madeenatur Rasool" (Birnin Manzon Allah) ko kuma Al Madeenatul Munawwarah (Birni abin haskakawa) wato ta haskaku da hasken Manzon Allah (saww) kenan. To bayan isowarsa sai dukkan lamuran garin suka koma hannunsa. Shine Sarki, shine Alkali, shine kwamandan yaqi, dama kuma shine jagoran addini ga dukkan masu rabo. Kuma ya fara gudanar da muhimman ayyuka guda uku kamar haka : 1. Ginin Masallacinsa. 2. Ha'da 'yan uwantaka atsakanin Sahabbansa na Madeenah (Al ansar) da kuma wadanda suka yiwo hijirah zuwa garesu (Al Muhajirun). 3. Qulla alkawuran zaman lafiya tsakanin al'ummarsa da kuma Yahudawan dake zaune acikin garin